EFCC Ta Sake Kama Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Ogun Da Wasu Mutane 2 Kan Zargin Almundahana

EFCC
EFCC

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) ta sake kama kakakin majalisar dokokin jihar Ogun, Olakunle Oluomo, kan zargin almundahana, jaridar Premium Times ta rahoto.

Mun dai ji cewa a ranar Alhamis da ta gabata, jami’an hukumar sun kama Mista Oluomo a filin jirgin sama na Murtala Mohammed da ke Lagas.

Sai dai kuma, an saki kakakin majalisar a daren ranar Juma’a sannan aka nemi ya dawo ofishin hukumar a ranar Litinin.

A lokacin da kakakin majalisar ya koma ofishin na EFCC a ranar Litinin, sai aka tsare shi.

Wata majiya ta ce Mista Oluomo da wasu mutane biyu da ake zargi suna tsare a hannun EFCC har zuwa karfe 9:43 na dare. Rahoton ya kuma ce daga kakakin majalisar har hadiminsa, Abdulgafar Adeleye, basu amsa kiran waya ba balle a ji ta bakinsu kan lamarin.

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here