Kada ku dauki nauyin sakonnin taya ni murna a ranar haihuwata – Shettima ya fada wa masu fatan alheri

Kashim Shettima 2 750x430

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya yi kira ga masu fatan alheri da su guji sanya sakonnin taya murna a gidajen jaridu, rediyo, talabijin da kafofin sada zumunta na zamani domin bikin cikarsa shekaru 60 da haihuwa.

Shettima ya yi wannan kiran ne a ranar Asabar a cikin wata sanarwa da Babban Mataimakin Shugaban Kasa na Musamman kan Kafofin Yada Labarai da Sadarwa, Mista Stanley Nkwocha, ya fitar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Kasa (NAN) ya ruwaito cewa Mataimakin Shugaban Kasa Shettima zai cika shekaru 60 da haihuwa a ranar 2 ga watan Satumba.

Ya bayyana cewa shawarar da ya yanke na daukar wannan babban mataki cikin sani da nuna cewa ya kamata hankalin jama’a ya karkata kacokan kan muhimman ayyukan ci gaban kasa maimakon shagulgula na kashin kai.

“Domin tabbatar da bin ka’ida, ina roko cikin girmamawa da kada a yi wani bikin taya murna a bainar jama’a, tarukan taya murna, ko tallace-tallacen fatan alheri a kafofin yada labarai na jaridu, rediyo, talabijin da kafofin sada zumunta na zamani,” in ji shi.

Maimakon taya shi murna ta hanyar gudanar da manyan bukukuwa ko biyan kudin tallace-tallace, Shettima ya bukaci masu fatan alheri da su karkatar da fatan alherinsu wajen yin addu’o’i ga Najeriya da kuma gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Ya yi kira da a yi addu’o’in samun nasarar gyare-gyaren tattalin arziki na gwamnatin, da samar da mafita mai dorewa ga kalubalen tsaron kasar da karfafa hadin kan kasa, zaman lafiya da ci gaban daukacin ‘yan Najeriya.
Shettima ya jaddada cewa ya kamata wannan lokaci ya zama mafari na yin tunani, nuna godiya da sabunta alkawarin yi wa kasa hidima, maimakon shagulgulan murnar cika shekaru na kashin kai. (NAN)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here