Ya kamata Trump ya nemi afuwa sakamakon kiran da ya yi wa Najeriya a matsayin “ƙasa mara ƙima” – Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa

L R Barau Jibrin and Donald Trump 750x430

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya soki shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, bisa kalamansa da ya kira Najeriya “ƙasa mara ƙima,” yana mai cewa wannan magana ba ta dace ba kuma ta saba da tsarin diflomasiyya.

Trump ya yi wannan furuci ne yayin taron manema labarai a fadar White House, inda ya yi gargaɗi cewa zai ɗauki matakin soja idan zarge-zargen kashe Kiristoci a Najeriya suka ci gaba.

Sanata Jibrin, a cikin wani faifan bidiyo da ya yadu yayin da yake jawabi ga matasan jam’iyyar APCongress, ya bayyana cewa kalaman Trump abin ƙyama ne kuma suna saɓawa dokokin ƙasa da ƙasa.

Ya ce babu wani shugaba daga wata ƙasa da ya dace ya yi barazanar kai hari ga wata ƙasa ba tare da bin tsarin doka ba, yana mai jaddada cewa kalaman Trump sun sabawa ƙa’idar haɗin kai tsakanin ƙasashe.

Sanata Jibrin ya bayyana cewa duk wanda ke da wata matsala da Najeriya, ya kamata ya bi matakan doka ta hanyar tuntuɓar Majalisar Ɗinkin Duniya domin samun matsaya, maimakon yin barazanar soja kai tsaye.

Ya kara da cewa kalaman shugaban Amurka sun nuna rashin girmamawa ga ƙasarmu, amma Najeriya ba za ta ji tsoro ba wajen faɗar gaskiya da kare mutuncinta a idon duniya.

Jibrin ya shawarci gwamnatin Amurka da ta bi hanyar diflomasiyya da girmamawa wajen warware duk wata matsala, yana mai jaddada cewa mutunta juna shi ne ginshiƙin dangantaka tsakanin ƙasashe.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here