Ganduje ya yi Murabus daga shugabancin APC

ganduje, kotu, APC, dakatar, tabbatar
Wata babbar kotu a jihar Kano ta dakatar da Dakta Abdullahi Umar Ganduje da ga shugabancin jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya. Mai shari'a Usman Malam...

Dakta Abdullahi Ganduje, ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban jam’iyyar APC na kasa.

Ganduje, wanda ya yi gwamnan Kano daga shekarar 2015 zuwa 2023, ya sanar da murabus ɗinsa ne nan take.

Ya zuwa yanzu ba a san hakikanin abin da ya sanya murabus din nasa ba, sai dai wani babban jigo a jam’iyyar ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce, “Eh gaskiya ne, ya yi murabus.”

Majiyoyi sun bayyana cewa tun da farko an kwashe kayan Ganduje daga ofishinsa dake sakatariyar jam’iyyar APC ta kasa, lamarin da ya kara rura wutar cece-kuce.

Wannan lamari dai, ya jefa shalkwatar jam’iyyar cikin rudani, inda ma’aikata da maziyarta suka kadu da wannan labari na bazata.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here