
Hukumar dake shirya jarrabawar manyan makarantun gaba da sakandare JAMB, ta ce ta rufe yin rigistar jarrabwar UTME bayan kara wa’adin da maku daya da tayi.
Shugaban sashin hurda da jama’a na hukumar, Dr Fabian Benjamin, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja ranar Talata.
Idon za’a iya tunawa a baya hukumar ta kara wa’adin yin rigistar da mako daya don bawa wadanda basu sami damar yin rigistar ba dama su yi.
Sanarwar ta kara da cewa sama da dalibai 1.6 million ne suka sam nasarar yin rigistar kafin cikar wa’adin da hukumar ta bayar.











































