Babu Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Ranakun Zaben 2023 – Yakubu

INEC Yakubu
INEC Yakubu

Shugaban Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), Farfesa Mahmoud Yakubu, ya ce za a gudanar da babban zaben 2023 kamar yadda aka tsara.

Ya ce za a gudanar da zaben Shugaban Kasa da na ’yan majalisun tarayya ranar 25 ga watan Fabrairu, sai kuma na Gwamnoni da na ’yan majalisar jiha ranar 11 ga watan Maris.

Ya bayyana hakan ne ranar laraba, lokacin da yake zantawa da ’yan jaridar Fadar Shugaban Kasa bayan ya kammala jawabi ga taron Majalisar Zartarwa ta Kasa da Shugaban Kasa Muhammadu buhari ya jagoranta a Abuja.

Farfesa Yakubu ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa za a gudanar da zaben ba tare da wani tarnaki ba.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here