Arsenal ta lashe kofin Premier League bayan shekaru 22

GettyImages 2256295097 750x430

Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta kawo karshen jiran shekaru 22 domin zama zakarun Premier League, a ranar Talata bayan da kungiyar Manchester City ta tashi 1-1 da Bournemouth.

City na bukatar nasara don kai fafatawar a ake kan wanda zai lashe gasar zuwa ranar karshe, amma Cherries sun tsawaita rashin nasarar su zuwa wasanni 17 a jere na gasar, wani tsari da ya tabbatar musu da buga gasar Turai a karon farko a tarihin kulob din.

Bayan kammalawa a matsayi na biyu a kaka uku da suka gabata, ‘yan wasan Mikel Arteta na Arsenal sun samu nasarar kawo karshen rashin lashe kofin na shekaru shida.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here