Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta kawo karshen jiran shekaru 22 domin zama zakarun Premier League, a ranar Talata bayan da kungiyar Manchester City ta tashi 1-1 da Bournemouth.
City na bukatar nasara don kai fafatawar a ake kan wanda zai lashe gasar zuwa ranar karshe, amma Cherries sun tsawaita rashin nasarar su zuwa wasanni 17 a jere na gasar, wani tsari da ya tabbatar musu da buga gasar Turai a karon farko a tarihin kulob din.
Bayan kammalawa a matsayi na biyu a kaka uku da suka gabata, ‘yan wasan Mikel Arteta na Arsenal sun samu nasarar kawo karshen rashin lashe kofin na shekaru shida.












































