Tinubu ya amince da bada lasisin kafa Jami’ar Sadarwa ta Tonnie Iredia, da wasu 10

tinubu 2 (1)

Majalisar zartaswa ta tarayya (FEC), a taronta na uku a ranar Litinin, ta amince da bayar da lasisi ga jami’o’i 11 masu zaman kansu a kasar nan.

Ministan Ilimi Dr Morufu Alausa ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai na fadar gwamnati bayan kammala taron na majalisar zartarwa FEC.

Ya ce jami’o’in da aka amince da su sun hada da: Jami’ar New City University, Ayetoro da ke Ogun, da Jami’ar Fortune, Igbotako a Jihar Ondo, da Jami’ar Eranova, Mabushi, da jami’ar Minaret Ikirun a jihar Osun sai kuma jami’ar Abubakar Toyin Oke-Agba a jihar Kwara.

Karin karatu: Jami’ar tarayya Kashere ta rattaba hannu kan yarjejeniyar haɗin gwiwa da Jami’ar Beaconhouse, Pakistan

Sauran su ne: jami’ar Southern Atlantic Uyo a jihar Akwa Ibom da Jami’ar Lens, Ilemona a jihar Kwara;l, da Jami’ar Monarch, Iyesi-Ota a jihar Ogun sai jama’ar Tonnie Iredia a Benin da jami’ar Isaac Balami a jihar Lagos da jami’ar Kevin Eze Mgbowo a Jihar Enugu.

Alausa ya ce gwamnatin shugaba Bola Tinubu ta himmatu wajen fadada harkokin ilimi da ababen more rayuwa, don haka ne ma ta amincewa da sabbin jami’o’in. (NAN)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here