Kwankwaso Ya Ziyarci Fadar Shugaban Kasa

WhatsApp Image 2025 07 22 at 00.49.58 750x430.jpeg

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigerian Peoples Party (NNPP), Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya je dakin taro na Banquet dake fadar shugaban kasa, Villa, Abuja, a ranar Litinin.

Jagoran Kwankwasiyyar ya halarci taron tattalin arzikin gandun daji na Najeriya na 2025, wanda kwamitin shugaban kasa kan tattalin arziki da hada-hadar kudi (PreCEFI) ya shirya.

Kamar yadda Aminiya ta ruwaito, Kwamlwaso bai gabatar da jawabi a wajen taron ba kuma bai yi magana da manema labarai a wajen taron ba.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here