Za mu fara gudanar da aikin kula da marasa lafiya kyauta ƙarƙashin NEMSAS- AKTH

WhatsApp Image 2025 08 29 at 14.40.52 750x430

Gwamnatin tarayya, ta ce, nan ba da dadewa ba hukumar bayar da agajin gaggawa ga mutanen da suka gamu da hatsari NEMSAS, za ta fara aiki a asibitin koyarwa na Aminu Kano AKTH.

Shugaban asibitin koyarwa na Aminu Kano Farfesa Abdurrahman Abba Sheshe, ne ya bayyana hakan ya na mai cewa tawagar hukuma ta kasa karkashin jagorancin Manajan shirin na NEMSAS Dakta Saidu Ahmed Dumbulwa, sun ziyarci asibitin domin tantance shirye-shiryen su.

Farfesa Sheshe ya bayyana cewa, “Wannan shiri ne mai matukar muhimmanci ga al’ummarmu, an yi shi ne ga talakawan kasa, waɗanda ba za su iya daukar nauyin sufuri da kula da lafiyarsu na gaggawa ba. “Mun yaba wa ma’aikatar lafiya ta tarayya da kuma shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa wannan shiri, kuma muna sa ran fara shi,” in ji shi.

SolaceBase ta ruwaito cewa Dr. Dumbulwa ya ce, Kano na da dabaru wajen kaddamar da shirin, wanda ke da nufin magance gibin da ake samu a fannin kiwon lafiya ta hanyar bullo da ayyukan daukar marasa lafiya masu inganci.

Ya bayyana cewa a karkashin shirin, mata masu juna biyu da yara wadanda hatsarin ya shafa, da sauran wadanda suka kamu da cutar za a kai su asibiti ba tare da biyan kudi ba, tare da yi musu magani kyauta a cikin sa’o’i 48 na farko.

Dakta Dumbulwa ya Kuma bayyana cewa jihohi 12 da manyan asibitoci 19 sun fara gudanar da wannan aiki, yayin da ake sa ran amincewa da AKTH nan ba da jimawa ba.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here