Shugaba kasa Buhari ya aike wa majalisa sunayen sababbin ministocin

Buhari signs sabo
Buhari signs sabo

Shugaban majalisar dattawan Najeriya Sanata Ahmed Lawan ne ya karanto sunayen sababbin ministocin da Shugaba Buhari ya aike wa majalisar a zaman da ta yi ranar Talata.

Sabbin ministocin sun hada da Ibrahim El-Yakub daga Jihar Kano, Umana Okon Umana (Akwa Ibom), Henry Ikechukwu Iko (Abia), Ademola Adegoroye (Ondo), Odum Odi (Rivers).

Sauran su ne Goodluck Nnana Opia (Imo) da kuma Joseph Ukama (Ebonyi ).

Sanata Lawan ya ce nan gaba za su tantance ministocin da aka mika musu domin tabbatar da su ko kuma akasin haka.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here