Cape Verde ta kasance ƙasa ta farko da ta kai zagayen gaba na ‘yan 16 bayan doke Mozambique da ci 3-0, a gasar kofin Afirka ta Afcon 2023 da ake gudanarwa a ƙasar Ivory Coast
Tsohon ɗan wasan Manchester United, wanda a yanzu ke taka leda a Rayo Vallecano, Bebe ne ya fara buɗe ragar Mozambique, bayan da ya ci ƙwallo mai ƙayatarwa a bugun tazara.
Daga nan Kaftin ɗin tawagar ƙasar, Ryan Mendes ya ƙara ta biyu.
Kafin daga bisani Kevin Pina ya ƙara ta uku daga wajen yadi na goma sha takwas.