Wasu ‘yan bindiga sun bukaci Naira miliyan 4 a matsayin kudin fansa domin a sako daya daga cikin masu yi wa kasa hidima (NYSC) da aka yi garkuwa da su a yankin jihar Zamfara.
Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da jami’an hukumar NYSC 8 a kan babbar hanyar jihar Zamfara a karshen makon da ya gabata.
Wadanda suka kammala karatun na baya-bayan nan an ce suna tafiya ne da wata motar bas ta Akwa Ibom daga Uyo, Akwa Ibom zuwa Jihar Sakkwato, domin shiga aikin yi wa kasa hidima a lokacin da motar ta su ta kama.
Emmanuel Etteh, mahaifin daya daga cikin wadanda harin ya rutsa da su, Glory Thomas, ya tabbatar wa gidan talabijin na Channels wannan sabon labari a wata tattaunawa ta wayar tarho ranar Juma’a. Etteh ya ce ‘yan fashin sun kira da lambar su domin sanar da shi game da sace ‘yar sa, inda suka bukaci ya biya Naira miliyan 4 domin a sako ta.