Shahararren Malamin Addinin Musuluncin nan na jihar Kano Sheikh Tijjani Bala Ƙalarawi, ya yi murabus daga mukaminsa na kasancewa mamba a kwamitin amintattu na masallacin Juma’a na Abdullahi Bayero, da ke unguwar Fagge.
Sheikh Tijjani Ƙalarawi ya bayyana hakan ne yau Litinin, ta cikin shirin wani gidan rediyo a Kano wanda Solacebase ta bibiya.
Malamin ya ce, ya dace ya yi murabus daga zama memba na kwamitin amintattu saboda gine-gine marasa kima da rabe-raben filayen da ake yi daga cikin filin masallacin.
Haka kuma ya ƙara da cewa, yin hakan rashin kulawa ce ga wurin bautar ubangiji.