Yanzu-Yanzu: Makinde ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a taron hadin gwiwar PDP da APM

Oyo State Governor Seyi Makinde

Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya bayyana kudurinsa na tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027 a karkashin jam’iyyar APM.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a wani taron siyasa da aka gudanar a Mapo Hall dake Ibadan, babban birnin jihar, a daidai lokacin da ake ci baga da samun tsarin siyasa a jihar wanda ya shafi bangarori na jam’iyyar PDP gabanin zaben 2027.

“Ni, Oluseyi Abiodun Makinde, Mai Girma, ina sanar da takarata ta Shugaban Tarayyar Najeriya,” in ji shi.

Da yake jawabi ga magoya baya a taron, Makinde ya bayyana shigarsa na shiga neman shugaban kasa a hukumance, wani mataki da ake sa ran zai sauya tattaunawar siyasa a cikin jam’iyyun adawa yayin da tattaunawa da hadin gwiwa ke karuwa gabanin zaɓlben fidda gwani na jam’iyyu da dabarun zabe gama gari.

Taron, wanda aka gudanar a daidai lokacin da ayyukan siyasa ke karuwa a cikin jam’iyyun adawa, ya samu halartar magoya baya da dama, da yawa daga cikinsu suka bayyana sanarwar a matsayin mataki mai muhimmanci a tafiyar siyasar kasa ta gwamnan Oyo.

Masana siyasa na cewa sanarwar ta Makinde cikin manyan masu neman takarar tun daga farkon fara al’amuran zaben shugaban kasa na 2027, musamman a cikin jam’iyyar PDP da hadakar jam’iyyun hadin gwiwar da ke tasowa.

Taron hadin gwiwar PDP da APM ma ya zama dandali na nuna hadin kai tsakanin wasu bangarori da ke halarta, inda shugabanni a taron suka yi kira ga karin hadin gwiwa da aiki tare gabanin zaben gaba.

Makinde ya jagoranci bangaren Taminu Turaki na PDP a Jihar Oyo zuwa sanya hannu kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna da APM a matsayin wani bangare na hadin gwiwar dabaru don zaben da ke tafe.

Gwamnan da Shugaban APM, Yusuf Dantalle, ne suka sanya hannu kan yarjejeniyar a madadin jam’iyyun biyu.

Karkashin yarjejeniyar, ‘yan takarar bangaren PDP da ke neman kujerar gwamna, Sanata, Majalisar Wakilai da Majalisar Dokokin Jihar ana sa ran za su tsaya a karkashin jam’iyyar APM maimakon PDP a zaben 2027.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here