Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya bar Abuja ranar Asabar zuwa birnin Landan.
Ana sa ran Osinbajo, zai wakilci Najeriya a wajen jana’izar marigayiya Sarauniya Elizabeth ta biyu.
Mai magana da yawun mataimakin shugaban kasa, Laolu Akande, ne ya sanar da hakan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitterranar Asabar.
Sakon yace Osinbajo, zai hadu da Sarki Charles, da dangin sarki da sauran shugabannin duniya a wasu tarurruka da liyafar da suka hada da taron kasashen biyu.