Kwana guda a fara gudanar da zaben gwamna a Jihar Kogi wani shugaban karamar hukuma ya rasu

IMG 20231110 WA0041 480x430
IMG 20231110 WA0041 480x430

Shuagaban karamar hukumar Lokoja ta jihar Kogi, Honorable Muhammed Danasabe, ya rasu.

Bayanai sun tabbatar da cewa Danasabe ya rasu ne a asibiti da misalign karfe 4 da mintuna 30 na asubahin ranar Juma’ar nan.

Jaridar Solacebase ta rawaito cewa mutuwar Shugaban karamar hukumar ta Lokoja na zuwa ne yayin day a rage kwana guda a kada kuri’a a zaben gwamnan Jihar ta Kogi, da aka shirya gudanarwa a ranar asabar 11 ga watan Nuwambar, shekarar da muke ciki ta 2023.

Iyalan marigayin sun ce za’a yi jana’idar sa kuma a binne shi a makabartar Musulmi dake Unguwan Kura bayan idar da sallar Juma’a.

Marigayin wanda ya kasance shugaban karamar hukumar Lokaja, ya rasu ya bar mahaifiyarsa, da matar sa daya da kuma Yara.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here