An Dakatar Da Dan Sandan Da Ya Harbe Lauya A Legas Daga Aiki

police 1 750x430 1
police 1 750x430 1

Hukumar Kula da Harkokin ‘Yan Sanda (PSC), ta dakatar da dan sandan da ake zargi da kashe lauya Bolanle Raheem da bindiga a Legas.

Dakatarwar na kunshe ne cikin  sanarwar da hukumar ta fitar ta bakin shugaban sashen yada labarai da hulda da jama’a, Mista Ikechukwu Ani, ranar Alhamis a Abuja.

Sanarwar ta ce dakatarwar da aka yi wa jami’in ta fara aiki ne take ba da bata lokaci ba.

Haka nan, hukumar ta ba da umarnin a yi binciken karshe kan badakalar domin daukar mataki na gaba.

Ani ya ce, bayan nazari cikin nutsuwa da hukumar ta yi wa lamarin ta aike wa Sufeto-Janar na ’Yan Sanda da wasika inda ta samu amincewarsa kan a dakatar da jami’in da lamarin ya shafa ba tare da bata lokaci ba.

Idan ba a manta ba, Aminiya ta ruwaito yadda dan sanda ya dirka wa marigayiyar bindiga ranar Kirsimeti a Legas, lamarin da ya ja hankalin jama’a a gida da wajen kasa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here