Gwamna Abba zai rantsar da Garo a matsayin mataimakin gwamna ranar Talata

WhatsApp Image 2026 04 22 at 00.53.02 720x430

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, zai rantsar da Mataimakin Gwamnan jihar, Murtala Sule Garo, a ranar Talata.

An tsara gudanar da rantsuwar ne a ranar Talata, a zauren Coronation Hall dake Gidan Gwamnati Jihar Kano, da karfe 11:00 na safe.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka wa gwamna kan harkokin yada labarai, Ibrahim Adam, ta ce ana sa ran masu ruwa da tsaki, ‘yan jam’iyya, da sauran al’umma za su halarci wurin rantsuwar.

Ana sa ran rantsar da mataimakin gwamnan zai samu halartar manyan jami’an gwamnati, masu ruwa da tsaki na siyasa, da kuma manyan baki daga fadin jihar da ma waje, yayin da gwamnatin ke ci gaba da ayyukanta na mulki.

Jaridar SolaceBase ta ruwaito cewa Majalisar Dokokin Jihar ta tantance Murtala Garo a ranar Litinin da ta gabata bayan samun nasarar tantancewa a gaban kwamitin mutum 12.

 

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here