‘Yan sanda sun fara gagarumin shirin daukar matakai domin dakile hare-haren ‘yan bindiga

'yan sanda, jami'i, zargin, kisan kai, neman, Anambra
Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta sanar da kama jami'inta, Insfekta Audu Omadefu mai lamba (AP No.362178) da laifin kisan kai. DSP Tochukwu Ikenga...

Rundunar ‘yan sandan kasar nan ta ce ta fara wani gagarumin shiri na daukar matakai domin dakile hare-haren ‘yan bindiga.

Hakan ya biyo bayan sace wasu ‘yan mata shida da aka yi a karamar hukumar Bwari da ke birnin tarayya a makon jiya.

Karanta wannan: Yan sanda sun yi fatali da sace matafiya a hanyar Abuja zuwa Kaduna

Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, ACP Muyiwa Adejobi ya fitar a ranar Lahadi ta ce, “Hedikwatar ‘yan sandan na ci gaba da hada kai don ganin an shawo kan lamarin tare da hana sake afkuwar lamarin.

Karanta wannan: NITDA zata samar da cibiyar kere-kere ta zamani a Kano

Idan dai za a iya tunawa, tun daga watan Disambar 2023, babu wani mako da ya wuce ba tare da rahoton hare-haren ‘yan bindiga da sace-sacen mutane ba, musamman a yankunan da ke makwabtaka da jihohin Kaduna da Neja da Nasarawa da kuma Kogi.

Al’ummomin da ke nesa kamar Kuduru da Gbaupe da Katari da Kawu da Arab Road a Kabwa da Dei-Dei da kuma wasu a Kuje sun fi shiga tashin hankali.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here