![Ana binciken dalilin yawan tashin gobara a jihar Kano Abba, Kabir, Yusuf, Kano, gobara, hukumar, kashe](https://solacebasehausa.com/wp-content/uploads/2023/10/Abba-Kabir-Yusuf-Kano-Governor-750x430.jpeg-696x399.jpg)
Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce tana ci gaba da bincike don gano musabbabin tashin gobara a wani rukunin shaguna abin da yayi sanadin konewarsu.
Al’amarin dai ya auku ne cikin dare a unguwar Zawaciki a karamar hukumar Kumbotso inda al’amarin ya yi sanadin asarar dukiya ta miliyoyin nairori.
Karin labari: “Zan mutu a hannun DSS” – Nnamdi Kanu
Bayanai na cewa ana yawan samun tashin gobara a jihar Kano, inda jami’in hulda da jama’ar hukumar kashe gobara a jihar Saminu Abdullahi, ya ce wutar na yawan tashi ne saboda amfani da wutar lantarki da ba bisa ka’ida ba.