Ambaliyar Ruwa Ta Kori Sama da Mutum Dubu Tare da Hallaka Kananan Yara a Kaduna

Floods in Jigawa
Floods in Jigawa

Wata mummunar ambaliyar ruwa ta raba mutane sama da dubu (1,000) da muhallansu tare da salwantar da rayukan yara biyu a Kafanchan da kauyukan da ke yankin karamar hukumar Jema’a (LGA) ta jihar Kaduna.

Madam Christy Usman, mataimakiyar shugabar karamar hukumar Jema’a, ta bayyana hakan a wata ziyara da kwamitin tantance tasirin ambaliyar ruwa na jihar Kaduna ya kai wa al’ummar da abin ya shafa a kudancin Kaduna a ranar Litinin.

Ta ce, ambaliyar ruwan da ta afkawa sassan garin Kafanchan, Jagindi, Atuku, Aso da Bade, ta kuma lalata gonaki, inda amfanin gonaki na miliyoyin naira ya tafi.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here