Gidauniyar Future Africa Leaders Foundation, FALF, ta ba da gudummawar Naira miliyan 500 ga ɗakin karatu na tsohon shugaban Najeriya,Olusegun Obasanjo da ke Abeokuta, jihar Ogun.
A cikin wata sanarwa da babban jami’in gudanarwa, COO, Loveworld, Fasto Ifeoma Chiemeka, ya fitar a ranar Talata, FALF kungiya ce ta Chris Oyakhilome Foundation International, COFI.
An bayar da gudummawar ne ga dakin karatu a ranar 3 ga watan Janairu, yayin da Obasanjo kuma ya karbi lambar yabo ta Future Africa ta 2022, wanda aka gudanar a ranar 31 ga Disamba, 2022.
Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa ya bayar da rahoton cewa gidauniyar ta ba wa matasa 10, daga kasashe daban-daban na Afirka kyautar dala dubu 10 kowannensu, sannan wanda ya lashe kyautar tauraro a cikinsu da karin dala 25,000 duk shekara.
Kyautar da aka bayar ita ce ga matasa su tallafa wa ayyukansu na raya Afirka daga yankunansu.









































