Yanzu-yanzu: Betta Edu ta isa Hukumar EFCC don amsa tambayoyi

Kungiyar,NCAC, shawarci, shugaba, Tinubu, Betta Edu
Kungiyar NCAC ta shawarci shugaba Bola Tinubu da kakkausar murya kan mayar da Misis Betta Edu a matsayin minista a gwamnatin Najeriya, musamman ma a...

Dakatacciyar ministar harkokin jin kai Dakta Betta Edu, ta isa hedikwatar Hukumar EFCC, domin amsa tambayoyi bisa zargin almundahanar Naira miliyan 585 a ma’aikatar ta.

Karanta wannan: Yanzu-yanzu: Tinubu ya dakatar da Betta Edu

Idan dai za’a iya tunawa dai a ranar Litinin ne shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Edu.

An zargi ministan da tura wasu kudade a wani asusu har Naira miliyan 585.

Wanda aka ce za’a yi amfani da shi ne don biyan tallafi ga marasa galihu a jihohin Akwa Ibom, Legas, Cross River da kuma Ogun.

Karanta wannan: Wani mutum ya mutu a Kano sakamakon kamawar wata Trailer da wuta

Edu dai ita ce minista ta farko da aka dakatar daga aiki tun bayan rantsar da mambobin majalisar zartarwa a watan Agustan shekarar da ta gabata.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here