Tinubu ya rattaba hannu kan kudirin maido da tsohuwar waka a matsayin doka

Gwamnatin, tarayya, ayyana, Laraba, matsayin, hutun, tunawa, dimokuradiyya
Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Laraba 12 ga watan Yuni a matsayin ranar hutu domin tunawa da ranar dimokuradiyya ta bana. A wata sanarwa da ma’aikatar...

Daga: Sunusi A. Dantalata Fagge

Shugaba Bola Tinubu ya amince da kudirin dokar wakar kasa na 2024 domin komawa tsohon taken kasar.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a wani zama na hadin gwiwa na Majalisar Dokokin kasar na bikin Jubilee na Azurfa na Jamhuriyyar Najeriya ta 4.

Ana sa ran shugaba Bola Tinubu a taron hadin gwiwa.

Karin labari: Babban sufeto janar na ‘yan sandan Najeriya ya nada sabon sakataren rundunar na kasa da kasa

Akpabio ya ce zaman da aka yi shi ne da farko don kaddamar da sabuwar wakar ta kasa, inda ya bayyana cewa shugaban kasar ba zai yi jawabi ba saboda ya tashi ya kaddamar da layin dogo na Abuja.

A baya dai Majalisar Dattawa da ta Wakilai sun amince da dokar sauya taken kasar daga “Tashi, Ya ku ‘yan uwa” zuwa “Najeriya, Mun gaishe ku” a tarukan daban-daban.

Tsohuwar waka mai suna “Nigeria, Mun gaishe ka” da aka yi a lokacin da Najeriya ta samu ‘yancin kai a ranar 1 ga watan Oktoba, 1960, ta maye gurbin wakar “Tashi, Ya ku ‘yan uwa”.

Karin labari: Buhari ya roƙi ‘yan Najeriya su sakawa gwamnatin Tinubu albarka

Lillian Jean Williams, Bature da ta zauna a Najeriya a lokacin da ta samu ‘yancin kai, ta rubuta wakokin “Nigeria, We Hail You,” yayin da Frances Berda ta tsara wakar.

Wakar ta taka rawar gani wajen samar da asalin kasa da hadin kan Najeriya a shekarun 1960 zuwa karshen 1970.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here