Atiku ya musanta janyewa daga siyasa, ya bayyana rahoton a matsayin labarin ƙarya

Atiku lalala

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya nuna damuwa kan abin da ya bayyana a matsayin yunƙurin wasu masu adawa da dimokuraɗiyya na haddasa ruɗani da rage ƙarfin da jam’iyyar ADC ke samu a halin yanzu.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya wallafa a shafin X a ranar Litinin, Atiku ya ƙaryata jita-jitar da ke yawo a shafukan sada zumunta cewa ya gana da masu ruwa da tsaki na ADC kuma ya yanke shawarar janyewa daga siyasa.

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP ya bayyana rahotannin da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta a matsayin marasa tushe kuma masu ruɗarwa.

Ya bayyana cewa bai gudanar da wata ganawa ta baya-bayan nan da masu ruwa da tsaki na ADC a matakin ƙasa ba, yana mai cewa ganawar da ya yi ta ƙarshe ita ce da wasu mambobin ADC a jihar Adamawa a ranar Alhamis da ta gabata.

Atiku ya jaddada cewa duk wata muhimmiyar shawara kamar janyewa daga harkokin siyasa ba za a sanar da ita ta hanyar jita-jita ko hanyoyin da ba su da tabbaci ba, sai ta hanyar ofishinsa na yaɗa labarai.

Ya kuma bayyana rahoton a matsayin wani ɓangare na shirya yaɗa ƙarya domin ruɗar da jama’a da rage ƙwarin gwiwa, yana mai cewa wasu na ƙoƙarin karkatar da hankalin al’umma.

Ya yi kira ga magoya bayansa, mambobin ADC da sauran ‘yan Najeriya masu kishin ƙasa da su yi watsi da wannan labari na ƙarya, su ci gaba da mai da hankali kan ƙoƙarin ceto ƙasar nan da sake gina ta.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here