Yan bindiga sun kashe mutum 9 ya yin da suke Mauludi a Katsina

0
Zamfara Killings

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Litinin ta tabbatar da cewa wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane tara a kauyen Rugar Kusa da ke karamar hukumar Musawa ta jihar.

Rundunar ‘yan sandan ta kuma tabbatar da cewa mutum 16 sun samu raunuka daban-daban a lokacin da maharan suka far wa musulmin da ke bikin Mauludi a ranar Lahadi.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Kakakin Rundunar yan sandan jihar Katsina, ASP Abubakar Sadiq-Aliyu ya fitar.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here