Da Dumi-Dumi: An shawo kan matsalar katsewar wutar lantarki a Najeriya

wutar, lantarki, kasa, maido, shawo kan, matsalar, katsewar, Najeriya
An samu daidaiton dawo da daukewar wutar lantarki a Najeriya. Idan ba'a manta ba SolaceBase ta bayyana katsewar wutar lantarki a Najeriya karo na...

An samu daidaiton dawo da daukewar wutar lantarki a Najeriya.

Idan ba’a manta ba jaridar SolaceBase ta bayyana katsewar wutar lantarki a Najeriya karo na hudu da yammacin ranar Asabar, abinda ya jefa al’ummar kasar cikin wani yanayi na daukewar haske.

Saidai a halin da ake ciki yanzu labari ya fita an samu nasarar shawo kan matsalar, kowanne lokaci daga yanzu za’a ci gaba da samun wutar lantarki a sassan kasar kamar yadda sanarwa ta fita daga Abdulazeez Abdullahi shugaban sadarwar kamfanin.

Karin labari: An sake samun katsewar wutar lantarki karo na 4 a Najeriya

Ya ku abokan ciniki masu daraja.

Muna nuna alhininmu da sanar da ku cewa katsewar wutar lantarki da ake fama da ita a cikin jihohin mu ya samo asali ne daga tushen Grid.

Matsalar ta faru ne da misalin karfe 3:10 na yamma.

Za’a dawo da wutar lantarki da zaran an kunna wutar lantarki ta ƙasa.

Muna neman afuwarku bisa kasancewar daukewar wutar.

Sa hannu:
Abdulazeez Abdullahi
Shugaban, Sadarwar Kamfanin.
6/07/2024

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here