Gwamnatin tarayya ta kira taron kwamitin sassa uku kan sabon mafi karancin albashi na kasa ta hanyar Hukumar Kula da Ma’aikata ta Kasa, wato NSIWC.
An shirya taron zaman ne don ranar Talata, 4 ga watan Yuni 2024.
Karin labari: NLC: “Yajin aikin ƙungiyoyin ƙwadago zai ƙara wa ƴan Najeriya wahala” – Jam’iyyar Labour
Kazalika, an dakatar da taron kwamitin da ya gabata ba zato ba tsammani a ranar 31 ga watan Mayu, lokacin da kungiyar da ke tattaunawa da kungiyoyin kwadago ta tashi, saboda gwamnati da kungiyoyi masu zaman kansu sun ki kara musu tayin Naira Dubu 60,000.
Cikakken labarin na tafe…