Uwargidan shugaban kasa, Oluremi Tinubu, ta ce mijinta, Bola Tinubu, ba matsafi ba ne, amma yana aiki don gyara kasar.
Da take jawabi a wajen taron coci-coci da aka gudanar domin tunawa da ranar samun ‘yancin kai a Abuja ranar Lahadi, Tinubu ta ce mijinta ba zai dora laifin a kan gwamnatocin baya ba.
Ta ce gwamnatin Tinubu ta gaji halin da ake ciki a kasa. “Duk abin da muka gada shi ne abubuwan da suka faru shekaru da yawa da suka gabata; ba mu zo mu dora laifin wata gwamnati ba sai dai gyara abin da ya lalace.”
“Mijina ba mai sihiri ba ne; zai yi aiki kuma na yi imani da fatan za mu samu zaman lafiya a kasar nan; mafi alheri har yanzu ya zo wurinmu,” in ji ta.













































