Yanzu-yanzu: Tinubu ya nada Taiwo Oyedele a matsayin minista

taiwo oyedele tinubu

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya nada Taiwo Oyedele a matsayin Karamin Ministan Kudi.

A cewar mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, tsohon Shugaban Kwamitin Shugaban Kasa kan Manufofin Kudi da Gyaran Haraji zai maye gurbin Doris Uzoka-Anite.

Shugaba Tinubu ya aike da sunan Oyedele zuwa Majalisar Dattawa domin tantancewa a cikin wata wasika da ya aika wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, kamar yadda Onanuga ya tabbatar a cikin wata sanarwa ranar Talata.

Uzoka-Anite zai koma Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsare ta Kasa a matsayin Karamin Minista, wanda shi ne mukaminsa na uku a wannan gwamnati.

A shekarar 2023, Tinubu ya nada Oyedele, wanda abokin hulda ne kan manufofin kudi kuma jagoran haraji na Afirka a PriceWaterhouseCoopers (PwC), a matsayin shugaban kwamitin gyaran haraji.

Oyedele mai shekaru 50 kwararre ne a manufofin jama’a, kuma akanta ne da masanin tattalin arziki.

Ya yi karatu a kwalejin fasaha ta Yaba inda ya samu babbar difloma (HND) a fannin lissafin kudi da kudi.

Oyedele ya kuma samu digirin BSc a fannin lissafin kudi da aka aiwatar daga jami’ar Oxford Brookes.

Ya kuma yi karatu a makarantar koyar da ilimin tsimi da tanadi da ke London, Yale, da makarantar Harvard Kennedy, inda ya kammala shirye-shiryen ilimi na manyan jami’ai.

Ministan ya shafe shekaru da dama yana aiki a PwC, inda ya fara aikinsa a cibiyar a shekarar 2001.

Farfesa ne a jami’ar Babcock da ke Jihar Ogun, sannan kuma malami mai ziyara ne a makarantar koyar da kasuwanci da ke Lagos.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here