Ƴan bindiga sun kashe basarake sun kuma ƙona gawarsa a jihar Imo

Nigeria Kidnappings Bandits deputy
Nigeria Kidnappings Bandits deputy

Wasu ƴan bindiga sun kashe babban basaraken garin Orsu Obodo da ke karamar hukumar Oguta a jihar Imo, Eze Victor Ijioma da kuma wazirin garin Mgbele shi ma a karamar hukumar.

Rahotanni sun ce maharan sun kashe shugabannin gargajiyar ne a hare daban-daban a jiya Alhamis.

Ƴan bindigar da ba a san ko su wanene ba zuwa yanzu sun hallaka babban basaraken ne a motarsa a garin Izombo kuma suka banka masa.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa wani da ya ga yadda abin ya faru wanda bai yarda a bayyana sunansa ba ya ce maharan sun tare basaraken na al’ummar Orsu Obodo a mahadar Umuamaka a garin Izombe da ke makwabtaka da nasu, inda suka hallaka shi.

Ya kara da cewa domin su tabbatar da ya mutu ne suka sanya wa gawarsa a cikin motar wuta.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa kakakin rundunar ƴan sanda a jihar Henry Okoye ya tabbatar mata da labarin kashe-kashen yau Juma’a.

Kuma ya ce Kwamishina ƴan sandan jihar Muhammed Barde ya kaddamar da binciken zakulo maharan.

Kashe-kashe da ƴan bindiga kan yi a jihar ta Imo sun karu tun bayan zabun da aka yi na jihar da kuma na tarayya.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here