’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 9, Sun Sace 20 A Kaduna

bandits
bandits

’Yan bindiga sun kashe wasu mutum tara da suka hada da ’yan banga hudu a unguwar Sabon Layi da ke Karamar Hukumar Birnin Gwari a Jihar Kaduna.

’Yan bindigar sun yi ta harbe-harbe tare da kashe mutum tara kafin su yi awon gaba da wasu sama da 20 tare da wasu dabbobi.

Idan dai za a iya tunawa, dakarun Operation Forest Sanity ta sojojin Najeriya sun yi wa wani kasurgumin shugaban ’yan bindiga a jihar, Isiya Danwasa da yaransa kwanton bauna tare da kashe shi.

Bayanai sun nuna cewa Isiya Danwasa ya yi kokarin tura daya daga cikin ’ya’yansa ya sayo wasu makamai da alburusai a garin Kaduna.

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here