Tinubu Ya Aike Da Ta’aziyyarsa Ga Iyalai Da Mabiya Na Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Giro Argungu

0
Sheikh Giro Argungu

Shugaban kasa Bola Tinubu ya aike da ta’aziyyarsa ga iyalai da mabiya na fitaccen malamin addinin Musulunci Sheikh Abubakar Giro Argungu wanda Allah Ya yi wa rasuwa a ranar Laraba.

Tinubu ya bayyana rasuwar shugaban addinin a matsayin rashi da ya wuce sauran al’ummar marigayin, a matsayin wanda ya shafi kasa baki daya, duba da irin gudunmawar da ya bayar ga kundin karatun addinin Musulunci.

Marigayin mai wa’azi ne a karkashin kungiyar Jama’atul Izalatul Bidi’a Wa’iqamatus Sunnah (JIBWIS).

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here