Tinubu Ya Aike Da Ta’aziyyarsa Ga Iyalai Da Mabiya Na Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Giro Argungu

Sheikh Giro Argungu
Sheikh Giro Argungu

Shugaban kasa Bola Tinubu ya aike da ta’aziyyarsa ga iyalai da mabiya na fitaccen malamin addinin Musulunci Sheikh Abubakar Giro Argungu wanda Allah Ya yi wa rasuwa a ranar Laraba.

Tinubu ya bayyana rasuwar shugaban addinin a matsayin rashi da ya wuce sauran al’ummar marigayin, a matsayin wanda ya shafi kasa baki daya, duba da irin gudunmawar da ya bayar ga kundin karatun addinin Musulunci.

Marigayin mai wa’azi ne a karkashin kungiyar Jama’atul Izalatul Bidi’a Wa’iqamatus Sunnah (JIBWIS).

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here