Hukumar kula da shige da fice ta ƙasa ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan zargin aikata ba daidai ba da ya shafi ɗaya daga cikin jami’anta, bayan wani rahoto da ya bayyana a internet wanda ke zargin jami’in da tsare wata ’yar Najeriya ba bisa ƙa’ida ba tare da cin zarafinta ta hanyar lalata.
A cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X a ranar Alhamis, ta ce an ja hankalinta zuwa wani rahoto a internet da ke zargin aikata munanan laifuka, ciki har da tsare yarinya ba bisa doka ba da kuma cin zarafi ta.
Hukumar ta bayyana zarge-zargen a matsayin masu tsanani, tana mai cewa duk wani aikin rashin ɗa’a daga jami’anta ba abin amincewa ba ne kuma ya sabawa ƙa’idodin aikinta na sana’a.
Hukumar ta bayyana cewa ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike, tare da tabbatar da cewa duk jami’in da aka samu da laifi zai fuskanci matakan ladabtarwa da na doka da suka dace.
Ta kuma jaddada cewa ba za ta kare ko ta goyi bayan duk wani jami’i da ya karya amincewar jama’a ko ya take haƙƙi da mutuncin mutane ba.
Sanarwar ta biyo bayan wani rahoto daga Gidauniyar aikin jarida ta bincike da ke zargin cewa an kama wata mata ’yar shekara 21 daga Jihar Akwa Ibom ta hannun wani jami’in shige da fice mai suna Isa Makama, inda aka tsare ta na tsawon kwanaki ba tare da bin tsarin doka ba.
Rahoton ya yi ikirarin cewa an tsare yarinyar a wani wuri na sirri maimakon wurin tsarewa na hukuma, tare da zargin cewa an rika cin zarafinta akai-akai yayin tsarewar, inda aka ce an sake ta ne kawai bayan wasu mutane sun shiga tsakani.
Hukumar shige da fice ta Najeriya ta ce ba ta tabbatar da cikakkun bayanan zarge-zargen ba, amma ta fara bincike domin gano gaskiyar lamarin da tabbatar da ɗaukar matakin da ya dace idan an tabbatar da laifi.












































