Gwamnatin Sokoto ta sanya dokar hana fita tsawon sa’a 24

images 10
images 10

Gwamnatin jihar Sokoto, ta sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 a ɗaukacin jihar sakamakon sauyawar zanga-zanga zuwa tarzoma.

Gwamnatin ta bayyana saka dokar ne a sanarwar da ta wallafa a shafinta na Facebook.

Haka kuma a cewar sanarwar dokar za ta fara aiki nan take daga lokacin wallafa ta.

A cewar gwamnatin jihar ta Sokoto ta ɗauki matakin ne domin dawo da zaman lafiya a jihar tare da tabbatar ingantuwar tsaro, bisa zanga-zangar da matasa suka yi a yau Asabar wadda ta koma tarzoma.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here