
Kimanin mutane 30 ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari kauyen Kwahaslalek da ke karamar hukumar Mangua ta jihar Filato a safiyar ranar Laraba.
An bayyana cewa wadanda harin ya rutsa da su yawancinsu mata ne da kananan yara, sun garzaya gidan wani shugaban al’umma da ke yankin ne a daren ranar Talata domin tsira da rayukansu sakamakon rikicin da ya barke da rana a garin Mangu inda ‘yan bindigar suka kewaye su tare da kashe su baki daya.
Karanta wannan: Kotu ta tasa keyar Danbilki Kwamanda zuwa Gidan Yari
Wani shugaba a yankin, Mark Haruna ya tabbatar da adadin wadanda suka mutu a Jos, babban birnin jihar a ranar Laraba.
Haruna ya ce, “Abin da ya faru a Sabon Gari da garin Mangu a jiya da rana, abin ya dame shi ne kawai don a kawar da hankalin jama’a daga kauyuka.
Karanta wannan: Badakalar Naira Biliyan 4: Tsohon Gwamnan Anambra Obiano ya isa Kotu
“A karo na biyu, kauyena Kwahaslalek a bayan sansanin NYSC, ya fuskanci hari da wasu ‘yan bindiga a jiya Talata. Sun zo ne da misalin karfe 12:30 na safe, suka kashe sama da mutane 25, galibi mata da kananan yara ne.”
Shugaban kungiyar ci gaban Mwaghavul, Joseph Gwankat shi ma ya tabbatar da kisan yana mai bayyana shi a matsayin rashin tausayi.
“Ban iya yin bacci a daren jiya ba sakamakon abin da ya faru jiya a garin Mangu da rana, yanzu dai an shaida min cewa an kai hari kauyen Kwahaslalek a daren jiya kuma an kashe mutane kusan 30″.












































