’Yan bindiga sun sace mata biyu da ’ya’ya shida na Dagacin Mutumbiyu a Jihar Taraba.
Bayanan da Aminiya ta kalato sun nuna ’yan bindigar sun kai hari gidan basaraken ne da ke Jalingo, babban birnin jihar, da tsakar dare a ranar Alhamis inda suka kwashi ahalin nasa.
Basaraken, Mai Shari’a Sani Muhammed (mai murabus), ba ya gidan nasa a lokacin da maharan suka kai farmakin.
Majiyarmu ta ce, maharan sun kira basaraken a kan ya same su don tattauna yadda za a saki iyalan nasa.
“An sace mata biyu da ’ya’ya shida na Dagacin Mutumbiyu da misalin karfe 1:00 na dare ranar Alhamis, kuma ana kokarin yadda za a kubutar da su,” in ji shi.













































