Kungiyar dalibai ta kasa (NANS) ta bayyana tsarin rashin aiki ba albashi da gwamnatin tarayya ta ayyana a kan kungiyar malaman jami’o’i da ke yajin aiki a matsayin abin takaici.
Kungiyar ta ce yin hakan basu amince da hakan ba, kuma ta yi kira ga gwamnati da ta biya malaman duk hakkoki da abin da suke nema.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kodinetan kungiyar na Kudu maso Yamma, Emmanuel Olatunji, a lokacin da daliban suke zanga-zangar a kan babbar hanyar Legas zuwa Ibadan.
Dalibai karkashin kungiyar NANS tun da farko sun fito kan tituna a ranar Talata, don nuna adawa da yajin aikin tare da yin tsinke kan babbar hanyar Legas zuwa Ibadan dake mahadar Shagamu.
“Muna kira ga gwamnatin Buhari da ta biya dukkan basussukan da malaman makaranta suke bi. Manufar “Babu Aiki Babu Biyan Kuɗi” wani makirci ne; saboda haka abin Allah wadai ne kuma ba za a yarda da shi ba ga dukkan miliyoyin dalibai a Najeriya!”, in ji sanarwar.
Sanarwar ta ce, “Mun fara daukar wannan mataki a yau kan yajin aikin ASUU. A bayyane yake cewa masu mulki ba su da kudin ilimi da muhimmanci ba kuma gwamnatin Buhari ta gaza wajen alkawurran da ta dauka na inganta ilimi.
“Kamar yadda yake a yau, babu wata babbar jami’a a Najeriya da ta yi fice a duniya! Duk da haka, waɗanda ake kira Ma’aikatan Gwamnati suna tafiya ko’ina cikin duniya, suna kashe biliyoyin kuɗi don tura ’ya’yansu zuwa ƙasashen waje don karatu.
“Mun sanya ido kan yadda dalibai suka fito harabar jami’a ta dandalinsu na sada zumunta da rubuce-rubucen jama’a.
“Malaman mu suna fama da wahalhalu da rashin ci gaban da muke fama da su. Gidajen ma’aikata sun yi muni kamar Dakunan kwanan dalibai. A Afirka ta Kudu, dakin gwaje-gwaje na Farfesa ya fi na kowacce jami’a a Najeriya kayan aiki.
“A kan hakane muka bayyana cewa: muna tare kan matsayin da ASUU ta dauka. Muna kira ga shugabannin ASUU da su yi taro da wuri-wuri don tattauna ayyukan hadin kai da kuma tsara mataki na nan gaba.













































