Malaman makarantun firaimare da ke Birnin Tarayyar Abuja sun dakatar da yajin aikin baba sai ta gani da suka tsunduma.
Rahotanni sun bayyana cewa tun farkon watan Janairu malaman suka fara yakin aikin, kan rashin biyansu mafi ƙarancin albashi da aka amince da shi na tsawon watanni 25, da kuma gaza aiwatar da kashi 40 cikin dari na alawus-alawus ɗinsu da shugabannin ƙananan hukumomin birnin shida suka yi.
Karanta wannan: Yajin aikin Malamai a Abuja: Wike ya zargi shugabanin kananan hukumomi
Labarin janye yajin aikin na cikin wata sanarwar bayan taro ta haɗin gwiwa da shugaban Ƙungiyar Malamai NUT ta fitar bayan kammala taronta na kwamitin koli da aka yi a Gwagwalada ranar Juma’a da maraice.













































