Hukumar NiMET ta yi hasashen samun hazo da ƙura na tsawon kwanaki uku Najeriya

Haze Thunderstorms

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya NiMet ta bayyana cewa za a samu hazo na ƙura a sassa daban-daban na Najeriya daga ranar Laraba zuwa Juma’a.

Hasashen yanayin da hukumar ta fitar a birnin tarayya Abuja ya nuna cewa a ranar Laraba, za a samu matsakaicin hazo na ƙura a yankin Arewa, inda nisan ganin ido a kwance zai kai tsakanin kilomita biyu zuwa biyar.

Rahoton ya nuna cewa za a samu raguwar ganin ido zuwa ƙasa da ko kuma daidai da mita dubu ɗaya a wasu sassan jihohin Katsina, Kano da Jigawa a duk tsawon lokacin hasashen.

Hukumar ta kuma yi hasashen samun matsakaicin hazo na ƙura a yankin Arewa ta Tsakiya a duk tsawon lokacin da rahoton ya shafa.

A yankin Kudu kuwa, hukumar ta bayyana cewa za a ga sararin samaniya mai haske tare da ɗan gajeren gajimare, inda ake sa ran samun ƙananan hadari da tsawa da ruwan sama kaɗan da rana ko da yamma a wasu sassan jihohin Legas, Bayelsa, Delta, Rivers, Cross River da Akwa Ibom.

Hukumar ta ƙara da cewa a ranar Alhamis, za a ci gaba da samun matsakaicin hazo na ƙura a yankunan Arewa da Arewa ta Tsakiya, yayin da a yankin Kudu za a ga sararin samaniya mai haske tare da ɗan gajeren gajimare, kuma akwai yiwuwar samun ƙananan hadari da tsawa da ruwan sama kaɗan a jihohin Ondo, Bayelsa, Rivers, Delta da Edo daga bisani a rana.

A ranar Juma’a, hukumar ta yi hasashen samun ɗan ƙaramin hazo na ƙura a yankin Arewa, yayin da za a ci gaba da samun matsakaicin hazo a yankin Arewa ta Tsakiya, sannan a yankin Kudu za a ga sararin samaniya mai haske tare da ɗan gajeren gajimare da yiwuwar samun ƙananan hadarin tsawa da ruwan sama kaɗan a jihohin Legas, Edo, Delta da Bayelsa.

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta gargaɗi jama’a cewa ƙurar za ta ci gaba da kasancewa a sararin samaniya, tare da ba da shawarar ɗaukar matakan kariya, musamman ga masu fama da cututtukan numfashi kamar asma, inda ta kuma shawarci direbobi su yi taka-tsantsan yayin tuki a lokacin ruwan sama.

NiMET ta yi kira ga kamfanonin jiragen sama su rika samun rahotannin yanayin jiragen sama kai tsaye daga hukumar domin tsara ayyukansu yadda ya kamata.

NAN

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here