Wata gobara da ta tashi a wurin wani cin abinci a Madrid babban birnin Spaniya, wadda ta yi sanadin mutuwar mutum biyu da jikkata wasu 10 na daban.
Wutar ta tashi ne a wajen cin abincin wani ɗan ƙasar Italiya da ke tsakiyar birnin kusa da Salamanca.
Waɗanda lamarin ya faru a kan idanunsu sun ce wutar ta tashi a lokacin da wani mai kai abinci ya ke ƙoƙarin kunna wuta a kan wani tire sai wutar ta tashi ta kama bango da rufin wurin.
A cewar masu aikin ceto, lokacin da wutar ta tashi, sai kwastomomi suka fara gudun tsira da rayuwarsu.
Yan sandan birnin sun fara bincike kan musabbabin tashin wutar.













































