Gobara ta hallaka mutum biyu a wurin sayar da abinci a Madrid

1682183562085
1682183562085

Wata gobara da ta tashi a wurin wani cin abinci a Madrid babban birnin Spaniya, wadda ta yi sanadin mutuwar mutum biyu da jikkata wasu 10 na daban.

Wutar ta tashi ne a wajen cin abincin wani ɗan ƙasar Italiya da ke tsakiyar birnin kusa da Salamanca.

Waɗanda lamarin ya faru a kan idanunsu sun ce wutar ta tashi a lokacin da wani mai kai abinci ya ke ƙoƙarin kunna wuta a kan wani tire sai wutar ta tashi ta kama bango da rufin wurin.

A cewar masu aikin ceto, lokacin da wutar ta tashi, sai kwastomomi suka fara gudun tsira da rayuwarsu.

Yan sandan birnin sun fara bincike kan musabbabin tashin wutar.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here