An fara taron G20 a India

g20 750x430.jpeg
g20 750x430.jpeg

A yau ake buɗe taron manyan ƙasashe masu ƙarfin tattalin arziƙi na G20, wanda a bana kasar Indiya ke karɓar baƙunci, sai dai biyu daga cikin ƙasashen da ke sahun gaba wato Rasha da China ba su halarci taron ba.

Tuni shugabannin ƙasashen suka fara taruwa a sabon ɗakin taron da aka gina a birnin Delhi.

Shugabannin za su tattauna kan batutuwa masu muhimmanci ciki har da matsalar sauyin yanayi, da matsalolin da ƙasashe masu tasowa ke fuskanta, sai dai ana sa ran yaƙin da Rasha ta ƙaddamar a Ukraine ya mamaye taron.

Da alama akwai kyakkyawan fata, ganin yawancin shugabannin kasashen sun amince da buƙatar Firai Ministan Narendra Modina ta gayyatar ƙungiyar Tarayyar Afirka domin shiga cikinsu su tashi daga G20 zuwa G21.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here