Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, ta sa ranar 7 ga watan Satumba a matsayin ranar da za ta fara sauraron karar da aka shigar da dan takarar shugabancin kasa a karkashin tutar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, kan zargin sa da ake da mallakatar takardun makaranta na bogi.
Wanda suka shigar da karar sun nemi kotun da ta dakatar da Tinubu daga shiga zaben 2023, saboda suna zargin sa da bada bayanan karya ga hukumar zabe ta kasa.













































