Wasu tsofaffin kwamishinonin Kano sun kai gwamnatin jihar ƙara kan kwace motocin aiki

FB IMG 1772120835515 1 750x430

Wani tsohon mamba na Majalisar Zartarwa ta Jihar Kano, AVM Ibrahim Umar (mai ritaya), ya garzaya Kotun Masana’antu ta Ƙasa reshen Kano, a madadin sauran tsofaffin kwamishinonin da lamarin ya shafa, kan takaddamar da ta taso game da mayar da motocin aiki.

Ƙarar mai lamba NICN/KN/14/2026 ta nuna AVM Ibrahim Umar (Rtd) a matsayin mai ƙara, inda ya shigar da ƙara a kan Babban Lauyan Jihar Kano da wasu mutum biyu.

A wata takarda da lauyan mai ƙara, Auwal Adam Ibrahim, ya rubuta a ranar 26 ga Fabrairu, 2026, ya zargi wasu da ya ce sun yi aiki bisa umarnin Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano da kutsawa gidan tsohon jami’in sojan saman tare da ɗauke motarsa.

Lauyan ya ce iyalan mai ƙarar sun firgita sakamakon lamarin, inda ya buƙaci a bayyana dalilin kutsen da aka yi da ƙarfi, sunaye da adireshin waɗanda suka shiga gidan, tare da mayar da motar cikin sa’o’i 48.

An aika kwafin wasiƙar ga Babban Lauyan Jihar Kano domin ɗaukar matakin da ya dace.

SolaceBase ta tuna cewa takaddamar ta biyo bayan murabus ɗin da wasu kwamishinoni suka yi, jim kaɗan bayan rahoton sauya sheƙar Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa jam’iyyar APC.

A wata wasiƙa mai kwanan wata 16 ga Fabrairu, 2026, mai lamba SSG/AGS/R/39/T.III, Ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar ya umarci tsofaffin kwamishinonin da abin ya shafa da su mayar da motocin aikin da aka ba su yayin da suke kan muƙami.

Sai dai a wata amsa ta haɗin gwiwa mai kwanan wata 17 ga Fabrairu, 2026, tsofaffin kwamishinonin sun yi nuni da tanade-tanaden Dokar Hukumar Tattara Kuɗaɗen Shiga da Kasafin Kuɗi ta 2023 (wadda yadda aka yi wa gyara), suna masu cewa motocin aiki na daga cikin sharuɗɗan aiki ga wasu rukunin masu riƙe da muƙaman siyasa da na gwamnati, ciki har da mambobin Majalisar Zartarwa ta Jiha.

Sun jaddada cewa an taɓa bai wa tsofaffin mambobi irin wannan gata a baya, tare da nacewa cewa haƙƙoƙinsu na da cikakken kariya a ƙarƙashin doka.

A wata sanarwar manema labarai da AVM Umar Ibrahim (Rtd) ya sanya wa hannu a madadin tsofaffin kwamishinonin, sun zargi gwamnatin jihar da ɗaukar matakin ramuwar gayya wajen neman a mayar da motocin.

Sanarwar ta yi zargin kutse da tsoratarwa, inda ta ce har da motocin sirri na matan aure aka kwashe yayin da iyalai ba sa gida.

Tsofaffin kwamishinonin sun ce sun nemi shigar kotu domin tabbatar da cewa an bi doka yadda ya kamata daga kowa da kowa, har da masu riƙe da madafun iko, tare da roƙon magoya bayansu da su kwantar da hankula har sai kotu ta fassara doka.

Sai dai wani jami’in gwamnati wanda ya nemi a sakaya sunansa ya watsar da zargin nasu, yana mai cewa ba su da wani haƙƙin kundin tsarin mulki na umartar gwamnati abin da za ta yi.

Jami’in ya bayyana cewa a irin wannan yanayi, gwamnati na iya sayar da motocin ga waɗanda aka ba su, ta ba su kyauta, ko kuma ta nemi a mayar da su.

A cewarsa, sayar da motocin yawanci na faruwa ne bayan kusan shekaru huɗu da amfani da su, alhali motocin da ake magana a kai an ba su ne a watan Mayu 2025, wato ƙasa da shekara guda da ta gabata.

Game da hujjar cewa an taɓa barin wani tsohon kwamishina ya riƙe mota, jami’in ya kwatanta hakan da “ɓarawon da aka kama yana sata yana korafin cewa wasu ba a kama su ba,” yana mai cewa abin da ya faru a baya ba zai rushe matakin da gwamnati ta ɗauka yanzu ba.

Zuwa yanzu dai lamarin na gaban kotu domin yanke hukunci.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here