Jirgin Saman Sojojin Najeriya Ya Yi Hatsari A Jihar Neja

NAF heluicopter crashed.jpeg
NAF heluicopter crashed.jpeg

Wani jirgin sojojin saman Najeriya mai saukar angulu, mai lamba MI-171 ya yi haɗari a jihar Neja. Lamarin dai ya faru ne da misalin ƙarfe 1 na ranar Litinin kusa da ƙauyen Chukuba da ke jihar, kamar yadda mai magana da yawun rundunar sojin saman Edward Gabkwet ya bayyana.

An bayyana cewa jirgin ya taso ne daga wata makarantar Firamare da ke Zungeru ta jihar Neja, wanda ya taso ne da zummar zuwa Kaduna.

Sai dai jim kaɗan bayan tasowarsa ne ya gamu da haɗari a kusa da wani ƙauye da ake kira Chukuba da ke ƙaramar hukumar Shiroro da ke jihar ta Neja. Rahoton Channels TV ya bayyana cewa har yanzu ba a tantance adadin mutanen da suke kan jirgin da asalin inda suka fito ba.

Karin bayani na tafe..

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here