‘Yan sanda sun kama kasurgumin mai garkuwa da mutane da ke fariya da kudinsa

John Lyon the Kidnapper
John Lyon the Kidnapper

‘Yan sanda sun kama wani da ake zargin rikakken mai satar mutane ne saboda fariyar da yake nunawa da dukiyarsa a shafukan sada zumunta.

Mutane sun san John Lyon ne, a matsayin ma’aikacin banki wanda a kullum rubuce-rubucen da yake wallafawa, na shawartar mutane su yi aiki tukuru kuma su kasance cikin aminci da taka-tsantsan.

Mai magana da yawun ‘yan sanda a jihar Bayelsa ya fada wa BBC cewa John Lyon yana tsare a hannunsu.

An mayar da mutumin da ake zargi zuwa Bayelsa bayan an kama shi a Abuja, babban birnin kasar, in ji Asimi Butswat.

A cewarsa, “Duk lokacin da suka samu kudin suna zuwa Abuja ne su yi ta rayuwar kece-raini”.

Hukumomi sun ce satar mutane don kudin neman fansa a kalla goma ake zargin gungun na John Lyon da aikatawa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here