Hedikwatar tsaro ta yi gargadi kan sanya kakin sojoji da kayan ado don yakin neman zabe da wasu ‘yan siyasa da sauran mutane ke yi ba tare da izini ba.
Mukaddashin Daraktan yada labarai na tsaro, Air Commodore Wap Maigida ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Abuja.
Maigida ya ce an baje hotunan yakin neman zaben wasu gwamnoni sanye da kakin soja, a wuraren da aka sani a jihohinsu.
Ya ce a fili wannan matakin ya sabawa doka kuma cin zarafi ne na baiwa fararen hula damar sanya kakin soji a lokacin atisayen soja.
A cewarsa, ya zama dole a sake bayyana cewa rundunar sojojin Najeriya a matsayinta na kwararrun cibiya, don haka ba za ta so a jawo ta cikin kowace irin salon siyasa ba.
Don haka, yana da kyau a shawarci ‘yan siyasa da sauran al’umma su daina amfani da kakin soja da kayan ado na soji don al’amuran siyasa da sauran abubuwan da suka faru daga yanzu.













































