‘Yan bindiga sun sake shiga Zaria, inda suka yi garkuwa da mutane 5

BD6C6E4C D918 4E34 822C 62E379620514
BD6C6E4C D918 4E34 822C 62E379620514

‘Yan bindiga sun sake kai hari gari Zaria, inda suka sace mutane 5 a Kasuwar Da’a dake yankin Dutsen Abba.

Wannan na zuwa ne awanni 24 bayan ‘yan bindiga sun kai wani hari akan titin Kaduna zuwa Zaria, inda suka kashe mutane 3 tare yin awon gaba da mutanen da ba a san adadin su ba.

Al’ummar yankin sun bayyana cewa da misalin karfe 1 na dare ‘yan bindiga suka shiga kauyen Dallatu inda suka sace mutane 2, daga bisani suka wuce kauyen kasuwae Da’a inda suka yi awon gaba da mutane 6, ciki harda kanan yara.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a safiyar lau laraba ‘yab bindigar sun sako kanan yaran da suka yi garkuwa dasu.

Zuwa yanzu rundunar ‘Yan Sanda bata ce komai ba.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here