Sama da ‘yan Boko Haram 150 ne suka rasa ransu a wani hari da sojijin saman Nigeria sukai kawai ‘yan kungiyar a dajin sambisa Kamar yadda wasu rahotanni suka tabbatar jirgin saman sojin Nigeria ya kai hari a ranar 21 ga watan Disambar wannan shekarar a wani sansanin ‘yan Boko Haram da ke Matari a karamar hukumar Bama ta jihar Barno.
Wata majiya a hukumar tsaron soji ta fadawa jaridar Zagazola cewa harin yayi mumunar illa ga maboyar ‘yan taddan da suke a yankin tafkin ChadZagazola.
cewa harin yayi mumunar illa ga maboyar ‘yan taddan da suke a yankin tafkin Chad.
Majiyar tace manyan kwamandojin kungiyar da suka hada da Babba Tukur, A kahid na cikin wanda suka rasa ransu yayin kai harin a sansanin Mantari da kuma na sansanin su na Maimusari.
Majiyar tace da ta samu wani kishin-kishin din kai harin ne bayan da ‘yan ta’addan suka gana da yan uwansu da suke zaune a Mantari, daga bisa ni suka karbi makamai da man mota suka koma. Su kuma sojojin sukai amfani da damar suka kai musu hari.












































